in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta zama kasa ta biyu da ta fi zuba jari ga kasashen waje
2017-06-08 13:40:31 cri
Taron cinikayya da ci gaba na MDD(UNCTAD) ya sanar a jiya Laraba cewa, yawan jarin da kasar Sin ta zuba a kasashen waje a shekarar 2016 ya karu, inda ta zama kasa ta biyu da ta fi zuba jari a ketare, duk da koma bayar tattalin arzikin da ake fuskanta a duniya.

James Zhan, darektan sashin zuba jari da kamfanoni na UNCTAD, ya ce yadda kasar Sin take kara zuba jari a kasashen waje ya nuna bukatar kamfanonin kasar ta kara taka rawa a kasuwannin duniya. Bisa yanayin da kasar ke ciki na kokarin aiwatar da shawarar "ziri daya da hanya daya", da habakar hadin gwiwa tare da sauran kasashe ta fuskar masana'antu, kasar Sin za ta ci gaba da zuba makudan kudade ga kasashen waje, in ji jami'in.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China