Jakadan Sin: Kare dabbobin daji muhimmin batu ne game da samun dawwamamman ci gaba
Jakadan kasar Sin a MDD ya bayyana kare dabbobin daji a matsayin muhimmin batu a bisa tsarin wayewar kan bil adama da samun dauwwamammen ci gaba, kana ya bukaci a dauki karin matakai wajen dakile cinikayyar dabbobin dajin ta haramtattun hanyoyi.
Liu Jieyi, wanda shi ne zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, ya yi kira ga kasa da kasa da su dauki matakai wajen kafa dokokin kawar da cinikayyar dabbobin dajin ta haramtattun hanyoyi, wanda kasashen Gabon da Jamus su ma sun yi makamancin wannan kira. (Ahmad Fagam)