in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 22 sun mutu a sakamakon rikicin da aka samu a gabashin kasar Afirka ta Tsakiya
2017-05-21 13:24:44 cri
Tawagar MDD dake kasar Afirka ta Tsakiya ta gabatar da rahoto a ranar 20 ga wata cewa, mutane 22 ciki har da fararen hula 17 ne suka mutu sannan wasu mutanen 36 sun samu raunuka a sakamakon rikicin da aka samu a birnin Bria dake gabashin Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya.

Tun daga ranar 15 ga wannan wata, dakarun anti-Balaka da kungiyar Popular Front for the Renaissance of Central Africa sun tada rikice-rikice a birnin Bria, wadanda suka haddasa mutane dubu 20 suka rasa gidajensu. Ya zuwa yanzu, a cikin mutane 22 da suka mutu a sakamakon rikicin, guda 17 fararen hula ne kuma saura 5 din membobin kungiyar anti-Balaka ne.

Tun daga watan Maris na bana, yanayin tsaro a kasar Afirka ta Tsakiya ya tsananta. Bisa kididdigar da kungiyar Red Cross a kasar ta yi, mutane fiye da 115 sun mutu a sakamakon rikicin da aka samu a birnin Bangassou dake kudu maso gabashin kasar. Kuma bisa kididdigar da MDD ta yi, mutane dubu 25 a cikin dukkan mazaunan birnin Bangassou dubu 35 suna bukatar taimakon jin kai. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China