in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR: 'Yan kasar Somaliya 30,000 ne suka koma gida daga Yemen
2017-05-19 21:23:10 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD UNHCR ta bayyana a yau Jumma'a cewa, kimanin 'yan kasar Somaliya 30,000 ne suka koma gida daga kasar Yemen tun lokacin da rikici ya barke a kasar a shekarar 2015.

UNHCR ta ce wasu karin 'yan kasar ta Somaliya na zuwa hukumar domin a tallafa musu ta yadda za su koma gida, inda ta nuna damuwa game da tsaro da rashin samun kayan agaji a Yemen.

Yemen dai ta kasance matsuguni da kuma zangon 'yan gudun hijira da bakin haure daga kahon Afirka da sauran sassan duniya. Yawancin 'yan gudun hijirar da ke kasar ta Yemen, kimanin kaso 91 ko 255,000 'yan gudun hijirar kasar ta Somaliya ne.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China