in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu 'yan kunar bakin wake sun gamu da ajalansu a Najeriya
2017-05-19 19:49:17 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, a kalla wasu maza 'yan kunar bakin wake guda uku ne suka gamu da ajalinsu yayin da suke kokarin kai hari sashen kwanan mata na jami'ar Maiduguri a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar

Wata majiyar 'yan sanda ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, daya daga cikin 'yan kunar waken yana dauke da bindiga kirar AK 47. Kuma a kalla boma-bomai biyu ne suka tashi a lokacin kai harin.

Wani ma'aikacin ceto da ke cikin wadanda ke taimakawa wadanda lamarin ya shafa, ya shaidawa manema labarai cewa, an yi wa ma'aikatan tsaron jami'ar guda hudu ciki har da masu aikin sa-kai magani, sakamakon raunin da suka ji. Koda yake babu wanda ya rasa ransa baya ga 'yan kunar waken.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China