in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya za ta samar da shirin diflomasiyya kan al'adu tsakaninta da Afrika ta Kudu don magance matsalar kyamar baki
2017-05-13 12:15:55 cri
Gwamnatin Nijeriya na shirin kaddamar da wani shirin diflomasiyya kan al'adu tsakaninta da gwamnatin kasar Afrika ta Kudu, da nufin kawo karshen nuna kyama da ake wa baki 'yan kasashen yammacin Afrika a Afrika ta kudu.

Yayin ganawarsa da jakadan Afrika ta Kudu a Nijeriya Lulu Mnguni, Ministan yada labarai da al'adu na kasar Lai Mohammed, ya ce shirin ya dace da kudurin shugaban kasar Muhammadu Buhari, kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da nufin kawo karshen kyamar baki.

Lai Muhammed ya kuma bayyana Nijeriya da Afrika ta Kudu a matsayin 'yan uwan juna, yana mai cewa, duk da rashin fahimta da su kan samu a wasu lokuta, kasashen biyu na da daddadiyar dangantaka.

A cewar gwamnatin Nijeriya, sama da 'yan Nijeriya 100 ne suka mutu ko suka jikkata yayin zanga-zangar kin jinin baki da ya barke a fadin Afrika ta Kudu a shekarar 2013.

Ministan ya bayyana shirin a matsayin ingantacciyar hanyar da za ta kawo karshen kyamar baki da karfafa fahimta tsakanin kasashen biyu. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China