in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Italiya ya kai ziyara a Libya
2017-05-07 13:00:51 cri
A jiya Asabar, ministan harkokin wajen kasar Italiya Angelino Alfano, ya gana da firaministan gwamnatin hadin gwiwar al'ummomin kasar Libya Fayes al-Sarraj a babban birnin kasar Libya, Tripoli, domin tattaunawa kan yadda za su hada kai ta fuskar yaki da 'yan ci rani ba bisa doka ba da dai sauran batutuwa.

Haka kuma, bisa labarin da aka samu, an ce, bangarorin biyu sun mai da hankali wajen yin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakaninsu bisa yaki da matsalar 'yan ci rani ba bisa doka ba, da kungiyoyi masu sa ran aikata laifuffuka da kuma yadda za a kiyaye tsaron yankin iyakar kasar da dai sauransu. Kana, Mr.Alfano ya nuna cewa, kasar Italiya za ta samar da taimako da goyon baya ga kasar Libya wajen gudanar da ayyukan dake shafar yankin iyakokin kasar da kuma kare tsaron kasar.

Sakamakon tabarbarewar yanayin tsaro a kasar Libya, an rufe ofishin jakadancin kasar Italiya tun daga ranar 15 ga watan Fabrairu na shekarar 2015. Sa'an nan, domin nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Libya ta fuskar sauyin mulki a kasa, an sake bude ofishin jakadanci na kasar Italiya dake kasar Libya a watan Janairu na shekarar bana, lamarin da ya nuna cewa, kasar Italiya ta kasance kasa ta farko cikin kasashen yammacin duniya wadda ta sake bude ofishin jakadancinta a kasar ta Libya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China