in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da tattaunawar tsaron hadin gwiwa game da shirin Ziri daya da hanya daya a birnin Bejing na kasar Sin
2017-05-05 09:47:36 cri
A jiya Alhamis ne jami'ai daga kasashe sama da 20 suka gudanar da tattaunawar tsaro ta hadin gwiwa game da shirin nan na "Ziri daya da hanya daya" a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Da ya ke karin haske game da tattaunawar, shugaban hukumar siyasa da harkokin da suka shafi doka na kwamitin tsakiya na JKS Meng Jianzhu, ya ce nauyi ne da ya rataya a wuyan dukkan kasashe su karfafa hadin gwiwar kasa da kasa a fannin tsaro, ta yadda za a magance duk wata barazanar tsaro da shirin Ziri daya da hanya daya ke fuskanta.

Meng ya kuma yi kira ga mahalarta taron, da su yi cikakken amfani da abubuwan da aka tattauna a taron ta hanyar musayar muhimman bayanai da inganta hadin gwiwar tsaro da kuma dokoki.

Jami'in ya ce, shirin ya kara samar da ci gaban hadin gwiwa a fannonin cinikayya da zuba jari da samar da muhimman kayayyakin more rayuwa, yana mai cewa, dandalin hadin gwiwa game da shirin na Ziri daya da hanya daya dake tafe, zai kara bunkasa hadin gwiwa a ragowar fannonin rayuwa

Bayanai na nuna cewa, ya zuwa yanzu dai sama da kasashe da kungiyoyin kasa da kasa 100 ne suka shiga shirin na Ziri daya da hanya daya, shirin da kasar Sin ta gabatar da nufin hade yankin Asiya da Turai da kuma nahiyar Afirka ta harkokin cinikayya da muhimman kayayyakin more rayuwar jama'a. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China