in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta zamo ta daya wajen zuba jarin kai tsaye a kasashen Afirka
2017-05-03 19:32:54 cri
Kasar Sin na kara yawan jarin kai tsaye da take zubawa a kasashen dake sassan nahiyar Afirka, matakin da a yanzu ya sanya ta zama ta daya a wannan fanni.

Wani rahoto da cibiyar kwararru ta Ernst & Young's mai helkwata a birnin London ta fitar, ya nuna cewa jarin da Sin ke zubawa kai tsaye ya habaka, kana yawan guraben ayyukan yi sun karu sakamakon hakan a nahiyar Afirka a shekarar 2016 da ta gabata.

Rahoton wanda aka fitar a Larabar nan, ya nuna cewa, tun daga shekarar 2005 da ta gabata, Sin ta zuba jari a ayyuka 293 a kasashen Afirka daban daban, wadanda kimar su ta kai dalar Amurka biliyan 66.4, baya ga guraben ayyukan yi 130,750 da hakan ya samar.

Jarin da Sin ke zubawa kai tsaye a nahiyar Afirka ko FDI a takaice, ya karade sassan samar da kayayyaki da masana'antu ke bukata, da na samar da hidima, da ma fanni sarrafa kayayyaki a masana'antu.

Har wa yau rahoton ya ce irin wannan jari na dada fadada a dukkanin sassan nahiyar Afirka, kama daga kasashe masu arzikin ma'adanai kamar Afirka ta kudu, da Najeriya da kuma Angola, ya zuwa masu fidda albarkatun gona kamar Kenya. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China