in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin tana kare 'yancin jama'ar kasar na bin addini bisa dokoki
2017-04-28 20:37:36 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Jumma'a 28 ga wata a nan birnin Beijing cewa, gwamnatin kasar Sin tana baiwa jama'arta 'yancin bin addini yadda dokoki suka tanada.

A kwanakin baya ne, kwamitin kula da 'yancin addini na kasar Amurka ya gabatar da rahoto na shekarar 2017, inda ya bada shawarar ci gaba da maida kasar Sin a matsayin kasar da aka fi maida hankali. Game da wannan batu, Geng Shuang ya bayyana cewa, jama'ar kasar Sin daga kabilu da sassa daban daban suna da cikakken 'yancin yin addinin da suka ga dama. Wannan kwamitin ya nuna bambanci ga kasar Sin kuma ta kyale ci gaban da Sin ta samu a fannin addini, kuma ya sha ba da rahotonni na shafa wa kasar Sin bakin fenti ta fannin 'yancin addini. Ya kamata ya girmama hakikanin halin da ake ciki kana ya yi watsi da ra'ayin kuskure, da daina tsoma baki a harkokin cikin gida na kasar Sin ta hanyar batun addini. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China