Yayin wani taron manema labarai, Hadimin Fadar Shugaban kasar Ibrahim Mahmoud Hamid, ya ce an kammala duk wata tuntuba da ake da nasaba da kafa sabuwar gwmnatin hadin kan al'umma.
Ibrahim Hamid ya kuma alakanta jinkirin da aka samu wajen sanar da kunshin sabuwar Gwamnatin, da niyyar da ake da ita na shigar da dukkanin jam'iyyun Siyasa da kungiyoyi masu dauke da makamai da suka shiga taron neman sulhu na kasar da aka kammala a watan Oktoban bara. (Fa'iza Mustapha)