in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabon tsarin musaya tsakanin al'ummomi zai inganta hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da Kasar Afrika ta Kudu
2017-04-26 09:47:56 cri
Mataimakiyar firayministan kasar Sin Liu Yandong, ta ce sabon tsarin musaya tsakanin al'ummomi da aka kaddamar, zai inganta huldar dake tsakanin kasar Sin da kasar Afrika ta Kudu.

Mataimakiyar firayministar ta bayyana haka ne lokacin da take ganawa da ministar harkokin wajen Afrika ta Kudu Maite Nkoana-Mashabane.

Ta ce kaddamar da wannan tsari a zo a kan gaba, wadda ta ce zai kara karfafa dangantaka dake tsakanin kasar Sin da Afrika ta kudu, ta hanyar kara samun goyon baya daga al'ummominsu.

Liu Yandong ta yi imanin cewa, shirin zai bada damar jin amon kasashen Afrika da sauran kasashe masu tasowa ga sauran sassan duniya, da kara bunkasa hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da Afrika ta kudu da ma nahiyar Afrika baki daya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China