An labarta cewa, bom ne ya fashe yayin da ake darasin ilmin kwamfuta. Ban da wannan, harin ya haddasa jikkatar 'yan makarantar 11, ciki hadda uku da suka galabaita.
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta Dagestan ta bayyana cewa, kawo yanzu dai, ana bin bahasin dalilin abkuwar harin.
Jamhuriyar Dagestan tana yankin Caucasia ta Tarayyar Rasha. Kuma dakarun haramtattun kungiyoyi kan ta da hankali a yankin, inda a kan samu tashe-tashen hankali da ayyukan ta'addanci. A kuma 'yan shekarun nan, gwamnatin Rasha ta kara karfin ta na yaki da haramtattun kungiyoyi a yankin.(Kande Gao)