Muhammad na 5, ya yi jawabi a gun bikin, yana mai cewa, shekarar 2017 shekara ce ta cika shekaru 60 da samun 'yancin kan kasar Malaysia. An kuma shaida cewa, mutane daga kabilu daban daban masu bin addinai daban, da al'adu daban, na zaune tare, da nuna girmamawa ga juna cikin lumana. Ya kuma yi fatan jama'ar kasar Malaysia za su ci gaba da hada kai da fahimtar juna, da daukar alhakin kare kasar su tare.
Don taya murnar kama aiki ga sabon jagoran kasar, kamfanin gidan waya na kasar Malaysia ya gabatar da kan sarki na musamman. Kaza lika gwamnatin kasar ta sanar da maida ranar 24 ga watan nan, a matsayin ranar hutu a dukkan kasar, kana za a gudanar da bikin nune-nune mai taken "sarkinmu" a dakin adana kayan tarihi na kasar, a ranar 2 ga watan Mayu. (Zainab)