in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan kasar Sin ya ce wani dandalin al'adu na kasar Girka yana da daraja
2017-04-24 11:26:41 cri
A wajen wani taron manema labaru da aka shirya a kasar Girka, wanda ministan harkokin wajen kasar Sin, mista Wang Yi, da takwaransa na kasar Girka Nikos Kotzias, suka halarta tare, ministan na kasar Sin ya yaba wa 'dandalin tsoffin kasashe masu al'adu' da kasar Girka ta shirya. A cewarsa, dandalin zai iya samar da taimako ga hadin gwiwar da ake yi bisa shirin "ziri daya da hanya daya", musamman ma a fannonin tunani da al'adu.

A cewar ministan na kasar Sin, yadda aka kirkiro dandalin "tsoffin kasashe masu al'adu" a kasar Girka yana da ma'ana sosai, bisa la'akarin da yanayin rashin tabbas da ake fuskantar a duniyarmu. Ta wannan hanya, a ganin ministan, za a samu gano wasu dabarun da aka taba aiwatarwa a tarihin dan Adam, wadanda za su taimakawa kokarin daidaita matsalolin da ake fuskanta a yanzu.

Wang Yi ya kara da cewa, kasar Sin ta gabatar da shirin "ziri daya da hanya daya" ne domin neman yayata akidar "hanyar siliki", wadda ta shafi kiyaye zaman lafiya da hadin gwiwa, da bude kofa, da hakuri, da koyon fasahar juna, da amfanar juna.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China