Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin Kenya Kanar Joseph Owuoth ya fitar, ta ce sojojin kasar sun gano wata matattarar kungiyar Al-Shabaab a jihar Lower Jubba dake kudancin Somaliya, inda suka kai musu farmaki a ranar 21 ga wata, al'amarin da ya yi sanadin halaka yayan kungiyar 52, tare kuma da kwace makamai da harsasai masu tarin yawa.
Kanar Owuoth ya ce, ba za a dakatar da fatattakar mayakan kungiyar Al-Shabaab ba, har sai an murkushe kafataninsu.(Murtala Zhang)