An gudanar da bikin sa hannu kan takardar tsara shirin bai wa Namibiya shinkafa tallafi a jiya Talata a birnin Windhoek fadar mulkim kasar ta Namibiya.
Bisa tanade-tanaden da ke cikin takardar, gwamantin kasar Sin za ta bai wa Namibiya taimakon shinkafa ton 2600 a wannan shekara.