Nan ba da dadewa ba ne ake sa ran gudanar da taron tattaunawa karo na 7 a tsakanin kasar Sin da kasashen Turai, game da manyan tsare-tsare a nan Beijing.
Dangane da hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana a yau Litinin 17 ga wata cewa, bangarorin 2 za su tsara shirin raya huldar da ke tsakaninsu a nan gaba a yayin taron. (Tasallah Yuan)