in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin wasannin Olympic na lokacin hunturu ya fara jarabawar domin daukar hayar ma'aikata daga kasa da kasa
2017-04-16 13:28:22 cri
A safiyar jiya Asabar, kwamitin shirya wasannin Olympic na lokacin hunturu ya yi jarabawar rubutu don daukar hayar ma'aikata a jami'ar horar da malaman koyarwa ta Beijing, inda mutane 760 wadanda suka cimma jarabawa ta farko suka halarci jarabawar ta wannan karo, domin neman guraben ayyuka 21.

Mahalarta jarrabawar sun zo ne daga yankunan kasar Sin, wasu kuma sun zo daga kasashen Rasha, Amurka da kuma Brazil da dai sauran kasashe da yankuna na duniya.

Tsawon lokacin jarabawa ya kai mintoci 210, inda aka yi jarrabawar kan fannonin binciken halin dan Adam, harsunan waje da kuma ilmin musamman dake shafar wasannin Olympic da sauransu.

Haka kuma, a wannan rana, kwamitin ya shirya wata jarabawa ta musamman, inda ya zabi mutane 76 da suka yi jarrabawar, domin nema ma'aikatan da za su dace wajen kula da ayyukan shirya wasannin Olympics na lokacin hunturu. Kuma, ma'aikatan da kwamitin yake neman a halin yanzu, ya kamata su taba yin irin wannan aiki a baya, kamar wanda ya taba shirya babbar gasa ta kasa da kasa, sannan kuma yake da kwarewa kan harsunan kasashen waje. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China