in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: ba wanda zai ci riba idan fada ya barke a zirin Koriya
2017-04-14 19:13:38 cri

Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya yi gargadin cewa, barkewar yaki a zirin Koriya, ba zai haifarwa kowa da mai ido ba. Mr. Wang yayi fatan daukacin kasashen duniya za su kai zuciya nesa domin kaucewa kara dagula al'amura.

Ministan wanda ya yi wannan tsokaci yayin zantawar sa da 'yan jaridu a Juma'ar nan bayan ya gana da takwaransa na Faransa Jean-Marc Ayrault, ya ce dangantaka na kara tsami tsakanin Amurka da Koriya ta Arewa. Kuma wannan yanayi ya dace da ja hankalin kowa.

Mr. Wang ya ce tun tuni Sin ke adawa da duk wani mataki na tada zaune tsaye, wanda ka iya rura wutar rikici. Kuma a bayyane take cewa, bisa tarihi warware takaddama ta hanyar shawarwari ita ce hanya mafi dacewa, a duk lokacin da aka samu rashin fahimtar juna.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China