Sin ta bukaci a karfafa hadin gwiwar kasashen yankin Great Lakes don tabbatar da tsaro
A yayin taron tattauna batutuwan yankin Great Lakes wanda kwamitin sulhu na MDD ya kira a ranar 12 ga wata, mataimakin zaunennen wakilin kasar Sin dake MDD Wu Haitao, ya bayyana cewa, kasar Sin tana son ganin hadin gwiwar kasashen dake yankin Great Lakes ta bangaren yi kokarin tinkarar 'yan tawaye, domin gudanar da ayyukan wanzar da tsaro.
Bugu da kari, Mr.Wu ya bayyana cewa, a halin yanzu, kasashen dake yankin Great Lakes suna fuskantar kalubaloli da dama dake shafar yaki da kungiyoyi masu dauke da makamai da kuma cimma burin samun dawamammen ci gaba da dai rauransu. (Maryam)