in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin aza harsashin gina babbar gada a Nijer
2017-04-07 16:56:28 cri
Jiya Alhamis, aka yi bikin aza harsashin gina babbar gada ta Janar Seyni Kountche a Niamey, babban birnin jamhuriyar Nijer, watau hakan na nufin za a fara aikin gina gadar a hukumance, kana aikin zai samu taimakon gwamnatin kasar Sin.

Shugaban kasar Nijer Mahamadou Issoufou, da jami'i mai kula da samar da kayayyakin aiki na kasar Kadi Abdoulaye da kuma jakadan kasar Sin dake jamhuriyar Nijer Zhang Lijun, sun halarci bikin.

A yayin da ya gabatar da jawabi, jakada Zhang Lijun, ya bayyana cewa, shirin gina babbar gadar ta Janar Seyni Kountche, shiri ne mafi girma daga cikin irin taimakon da kasar Sin take samarwa a jamhuriyar Nijer, kuma bisa hasashen da aka yi, gaba daya za a kashe kudin Sin RMB miliyan 557, kuma za'a kammala aikin gadar mai nisan kilomita 3.7 dake kudu maso yammacin birnin Niamey cikin watanni 36.

A nasa bangare, shugaba Issoufou ya nuna matukar godiya ga kasar Sin kan taimakon da ta samarwa kasarsa, ya kuma jaddada cewa, gina babbar gadar za ta yi matukar tallafawa al'ummomin kasar, musamman wajen inganta bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'umma a kasar ta Nijer daga dukkan fannoni. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China