Sanarwar ta bayyana cewa, samun zaman lafiya mai dorewa a dukkan fannoni shi ne zabi mafi dacewa ga kasashen Larabawa, kuma kasashen za su ci gaba da kokarin sake gudanar da shawarwarin shimfida zaman lafiya a tsakanin Palesdinu da Isra'ila, da kawo karshen rikicin dake tsakaninsu.
Kaza lika sanarwar ta bayyana cewa, shirin kafa kasashe biyu hanya ce daya tilo, ta cimma samun tsaro da zaman lafiya tsakanin Palestinu da Isra'ila.(Zainab)