in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar WFP ta bullo da muhimmin shirin kawar da yunwa a kasar Sin
2017-03-29 13:07:46 cri
Shirin wadata abinci na MDD WFP, ta bullo da wani muhimmin shiri kan kawar da matsalar yunwa daga shekara ta 2017 zuwa ta 2021 a jiya Talata a nan birnin Beijing, shirin zai yi kokari tare da ma'aikatar aikin gona ta kasar Sin da sauransu, domin kawar da yunwa a fadin duniya, da cimma burin samun ci gaba mai dorewa.

A karkashin wannan muhimmin shiri, nan da shekaru biyar masu zuwa, hukumar WFP zata nuna goyon-baya ga gwamnatin kasar Sin, wajen inganta samar da abinci mai gina jiki ga daliban dake yankunan karkarar kasar, da tallafawa manoma masu fama da kangin talauci, da kara karfin farfado da yankunan dake yawan fuskantar barazanar bala'u.

Har wa yau kuma, shirin WFP zai nuna goyon-baya ga kasar Sin, da ma sauran wasu kasashen dake tasowa, don su samu damar bayyana yadda suke inganta tsaron abinci da rage talauci.

A nasa bangaren, wakilin hukumar WFP dake kasar Sin Qu Sixi ya bayyana cewa, a halin yanzu hukumar na yin kwaskwarima ga ayyukanta, a wani kokari na taimakawa kasar Sin, da sauran kasashen dake tasowa, cimma burin samun ci gaba mai dorewa a shekara ta 2030.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China