in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kwarya-kwaryan taron ministocin harkokin wajen kasashen kawancen Larabawa
2017-03-28 10:58:24 cri
Jiya Litinin ne, aka kaddamar da taron ministocin kula da harkokin waje na kasashen kawancen kasashen Larabawa karo na 28 a kasar Jordan, inda aka gudanar da shawarwari kan wasu muhimman batutuwan dake yankin.

Shugaban taron, kana ministan harkokin wajen Jordan, Ayman Al-Safadi ya yi jawabi, inda ya ce, batun Falasdinu batu ne mafi muhimmanci a gaban kome, haka kuma ya ce, kawo karshen mamayar yankunan Falasdinawa bisa shirin kasashen biyu, wani babban sharadi ne na wanzar da zaman lafiya da tabbatar da kwanciyar hankali a yankin.

Ayman Al-Safadi ya kuma jaddada muhimmancin daidaita batun Siriya ta hanyar shawarwari.

Dangane da sauran wasu batutuwan dake gaban kasashen Larabawa, ciki har da batun Libiya da batun yaki da ayyukan ta'addanci, Ayman ya ce, ya kamata a farfado da zaman lafiya da samun sulhu a fadin Libiya. Haka kuma ya ce, ya zama tilas a murkushe ayyukan ta'addanci, domin kare fararen hula.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China