Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, a Litinin din nan ta sake nanata cewa, tsibirin Diaoyu, da kananan tsibiran da ke kewayensa, yankin kasar Sin ne tun fil azal.
Ta ce kasar Sin ta bukaci kasar Japan da ta girmama tarihi, da hakikanin abubuwa, ta dakatar da ita da hargitsi a batutuwa da suka shafi mallakar wadannan tsibirai. (Tasallah Yuan)