in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron kolin IGAD zai nazarci makomar 'yan gudun hijirar Somali miliyan guda
2017-03-21 10:32:12 cri
Kungiyar raya cigaban kasashen gabashin Afrika (IGAD), zata gudanar da taron koli na kasa da kasa a ranar Asabar mai zuwa, domin tattaunawa game da makomar 'yan gudun hijirar Somali miliya 1, wadanda yakin basasa ya tilastawa ficewa daga muhallansu shekaru 20 da suka gaba, kuma sun jima suna fama da wahalhalun rayuwa, kamar yadda masu shirya taron suka tabbatar da hakan.

Gwamnatin kasar Kenya, da ofishin kula da yan gudun hijira na MDD (UNHCR) da IGAD, sun bayyana cikin wata sanarwa cewa, taron kolin na birnin Nairobi, zai nazarci dukkan batutuwan da suka shafi rikicin shiyya, da nufin lalibo bakin zaren warware matsalolin rikice rikice da 'yan gudun hijirar Somali suka jima suna fuskanta, kasancewar a halin yanzu sun yanke kudirin komawa garuruwansu na ainihi domin cigaba da sabuwar rayuwa.

Masu shirya taron sun ce, karuwar rikicin siyasa gami da tsanantar yanayin tsaro da ake samu a Somali, kana da yawaitar fargaba a yankunan dake karbar bakuncin 'yan gudun hijirar, ya tilasta nemo hanyoyi masu inganci na warware matsalolin da suka shafi 'yan gudun hijirar na Somali.

Hukumomin ba da agaji da jami'an gwamnatoci sun bayyana cewa, 'yan gudun hijirar Somali miliyan biyu ne suka kauracewa matsugunansu, kuma wannan shi ne adadin mafi muni a duniya wanda rikicin siyasa ya jefa al'ummar cikin yanayin matsin rayuwa wanda ya shiga shekaru na 30.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China