Mr. Mahamat ya kuma jinjinawa tsohon shugaban hukumar ta CAF Issa Hayatou, bisa gudummawar da ya baiwa hukumar,da ma ci gaban kwallon kafa a Afirka cikin tsawon shekaru.
Kafin zaben sa, Ahmad shi ne shugaban hukumar kwallon kafar kasar Madagascar, ya kuma kada Issa Hayatou wanda ke rike da jagorancin CAF din da kuri'u 34, yayin da Hayatou ya samu kuri'u 20, yayin zaben da aka kada a zaman hukumar ta CAF na 39, wanda ya gudana a helkwatar AU dake birnin Addis Ababan kasar Habasha.