in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
OPEC da kasashe masu arzikin mai sun sake nanata ci gaba da rage hako man fetur
2017-03-08 21:05:56 cri
Jiya Talata ne kungiyar kasashe masu fitar da man fetur wato OPEC da kuma wasu kasashe masu arzikin mai wadanda ba mambobin kungiyar OPEC ba suka sake nanata cewa, za su ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar rage hako man da suka cimma a karshen shekarar bara, a kokarin daidaita farashin man fetur a duniya.

Bisa yarjejeniyar da suka cimma, daga watan Janairun bana zuwa karshen watan Yunin bana OPEC za ta rage hako gangunan danyen mai miliyan 1 da dubu 200 a kowace rana, yayin da kasashe 11 masu arzikin mai wadanda ba mambobin kungiyar OPEC ba za su rage hako gangunan danyen mai dubu 558 a kowace rana. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China