in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da Amina Mohammed a matsayin mataimakiyar sakatare janar na MDD
2017-03-01 09:14:43 cri

An rantsar da Amina Mohammed, tsohuwar ministar muhalli ta Nigeria a matsayin mataimakiyar sakatare janar na MDD a jiya Talata.

A jawabinsa na maraba, sakatare janar na majalisar Antonio Guterres ya ce, ya yi matukar farin ciki da ta amince ta yi aiki da shi.

Da take ganawa da manema labarai jiya da safe, Amina Mohammed ta ce, za ta mai da hankali wajen taimakawa sakatare janar din sake fasalin muradun ci gaba masu dorewa a majalisar.

Aikinta na farko shi ne bude sashen majalisar kula da tattalin arziki da zaman takewa na bana, a wani bangare na ayyukan samar da ci gaba.

Amina Mohammed ta kasasnce mace ta biyu 'yar Afrika da aka nada matsayin mataimakiyar sakatare janar na MDD. Mace ta farko ita ce Asha-Rose Migiro, 'yar kasar Tanzania, wadda ta kasance kan mukamin daga 2007 zuwa 2012, karkashin shugabanci Ban Ki-moon. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China