in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Miyagun kwayoyi na haifarwa kasashen yammacin Afirka hasarar dukiya
2017-02-22 09:59:09 cri
Shugaban sashin yammaci da tsakiyar Afirka na ofshin yaki da miyagun kwayoyi da aikata laifuka na MDD (UNODC) Pierre Lapaque, ya ce a kowace shekara, miyagun kwayoyi na haifarwa hukumomin lafiya, da na samar da ayyukan yi dake kasashen yammacin Afirka hasarar dukiyoyi da yawansu ya kai fiye da dalar Amurka miliyan 1300.

Mista Lapaque ya yi wannan furuci ne a shekaran jiya Litinin, yayin taron kara wa juna sani kan batun kandagarki, da kawar da jarabar shan kwaya a yammacin Afirka, wanda ya gudana a birnin Abijan, fadar mulkin kasar Ivory Coast. Ya ce a baya yankin yammacin Afirka ya kasance yanki da masu jigilar miyagun kwayoyi ke amfani da shi wajen safarar kwayoyin, amma a shekarun baya bayan nan, yankin ya fara zama wuri da ake sarrafa kwayoyin tare da amfani da su. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China