in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi shawarwari tsakanin ministocin harkokin wajen kasashen Sin da Mongoliya
2017-02-20 20:39:20 cri
A yau Litinin ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Mongoliya a nan birnin Beijing.

A yayin shawarwari, Wang ya bayyana cewa, kasar Mongliya ta sake nanata matsayinta na martaba manufar Sin daya tak a duniya, tare kuma da girmama muradun Sin game da batutuwan da suka shafi yankin Tibet da dai sauransu, wannan na da ma'ana sosai ga bunkasa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Wang ya kara da cewa, kasarsa na son bullo da wani shirin cudanya tsakanin manyan jami'an kasashen biyu, da karfafa hadin kai bisa manyan tsare-tsare, da ciyar da hadin kai a fannonin samar da kayayyaki, zuba jari da muhimman kayayyakin more rayuwa da dai sauransu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China