in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwararru: Dokar hana shiga Amurka ta nuna wariya ne ga alummar musulmi
2017-02-02 13:15:37 cri
Wasu kwararru kan aikin kare hakkin dan adam na MDD sun fitar da wata sanarwa ta hadin gwiwa a jiya Laraba, inda suka bayyana cewa, dokar da shugaban Amurka Donald Trump ya sanyawa hannu, ta saba wa dokar hakkin bil adama ta kasa da kasa, dokar MDD wadda ta baiwa dan adam 'yancin yin walwala ba tare da nuna masa wariya ko bambancin launin fata, ko bambancin yanki, ko na addini ba.

Sanarwar ta kara da cewa, wannan umarni tamkar nuna wariya ne saboda bambancin kasa da ya nuna, kuma hakan zai haddasa kara nuna kyama ga mabiya addinin musulunci. Sanarwar dai wanda wakilai na musamman na MDD suka ratattabawa hannu, da suka hada da wakilin musamman na sahen kula da bakin haure, Francois Crepeau; da na sashen nuna wariya Mutuma Ruteere; da na kare hakkin dan adam da yaki da ta'addanci, Ben Emmerson; da sashen muzgunawa, Nils Melzer; da kuma na sashen 'yancin addini, Ahmed Shaheed.

A yayin da shugaban Amurka ya bada umarnin dakatar da shirin 'yan gudun hijira na kwanaki 120, masanan sun bayyana cewa a daidai wannan lokacin da duniya ke fuskantar karuwar 'yan gudun hijira mafi yawa da ba'a taba fuskantar irinsa ba tun bayan yakin duniya na biyu, wannan babban koma baya ne musamman ga mutanen dake neman kariya ta kasa da kasa.

Kwararrun sunce wajibine Amurkar ta samar da kariya ga mutanen da rikici ya daidaita.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China