in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Cote d'Ivoire da sojojin masu bore sun cimma yarjejeniya
2017-01-15 13:52:40 cri
Bayan da aka yi shawarwari a dogon lokaci, gwamnatin kasar Cote d'Ivoire da sojojin masu tada bore sun cimma matsaya a daren ranar 13 ga wannan wata. A halin yanzu, hankula sun kwanta a sassan kasar daban daban na kasar ta Cote d'Ivoire.

An ce, a madadin gwamnatin kasar, ministan tsaron kasar ya halarci shawarwarin, a karshe dai an cimma daidaito tare da sojoji masu yin bore. Kana sojojin da dama sun tabbatar da cewa, bangarorin biyu sun daddale yarjejeniyar zaman lafiya.

Wani masani game da harkokin gwamnatin kasar Cote d'Ivoire ya bayyana cewa, sojoji masu tada rikicin sun amince da komawa sansanoninsu, kana an dakatar da harbar bindiga a birnin Bouake. Ya ce, bisa yarjejeniyar da aka daddale, ko wane sojojin zai samu kudi dala dubu 19 daga gwamnatin kasar. Wani wakilin sojojin dake halartar shawarwarin ya bayyana cewa, za a fara biya kudin tun daga ranar 16 ga wannan wata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China