in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a bude taron shekara-shekara na dandalin tattaunawar tattalin arzikin duniya a ranar 17 ga wata
2017-01-10 19:46:57 cri
Daga ranar 17 zuwa 20 ga wannan ne wata za a bude taron shekara-shekara na dandalin tattaunawar tattalin arzikin duniya a Davos na kasar Swizerland, inda baki sama da 3000 daga kasashe fiye da 100 za su halarci taron, ciki har da shugabanni fiye da 2000 a fannonin siyasa da kasuwanci.

A yayin taron manema labaru da aka shirya a yau a Talata a nan birnin Beijing, darektan zartaswa na dandalin, kuma babban wakilin dandalin dake Sin David Aikman ya bayyana cewa, an shirya taron ne da nufin yin kira ga shugabanni a fannoni daban daban da su gabatar da sabbin shawarwari, tare kuma da daukar hakikanin matakai, don kara imanin al'umma kan makomar bunkasuwar duniya a nan gaba.

Ana saran a yayin taron za a mayar da hankali kan jerin kalubaloli masu tsanani da duniya ke fuskanta a shekarar 2017, ciki har da yadda za a karfafa tsarin hadin kan duniya, don tinkarar tasirin da dunkulewar tattalin arzikin duniya ke haifarwa, da yadda za a sake farfado da tattalin arzikin duniya, don warware matsalolin raguwar saurin ci gaban tattalin arziki da batun matsalar rashin ayyukan yi, kana da yadda za a kawar da matsalar rashin hangen nesa, son kai da cin hanci, don kara kyautatta halin kasuwanni, da kuma yadda za a share fage game da juyin juya halin masana'antu karo na hudu da dai sauransu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China