Benin: Kungiyoyin kwadago sun yi allawadi da sayar da kamfanonin gwamnati guda hudu
Sakatarorin kungiyoyin kwadago biyar da tarayyar kungiyoyin kwadago bisa ga guda bakwai da kasar Benin take da su sun yi allawadai a ranar Talata a birnin Cotonou, a yayin wani taron gangami, matakin gwamnatin Benin na sayar da kamfanonin kasar guda hudu dake karkashin ma'aikatar noma, kiwo da kamun kifi. A cewar hukumomin Benin, ayyukan wadannan kamfanoni hudu mallakar gwamnati ba su taka rawar a zo a gani ba sabanin sasshen darektocin ma'aikatu na jihohi, da cibiyoyin bunkasa noma da hukumomin yankunan kasar na bunkasa noma da aka kafa. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku