in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kebe wa bangaren ilimi Yuan triliyan 3.6 a shekarar 2015
2016-11-11 09:37:43 cri

Gwamnatin kasar Sin ta kebe wa sashen ilimin kasar tsabar kudi har Yuan triliyan 3.6 a shekarar 2015, wato karin kaso 10 cikin 100 ke nan a ko wace shekara.

Wata sanarwar hadin gwiwa da ma'aikatun ilimi da na kudi da kuma hukumar kididdiga ta kasar suka fitar a jiya Alhamis, ta nuna cewa,Yuan triliyan 2.92 na wadannan kudade sun fito ne daga baitulmalin kasar, adadin da ya kai kaso 4.26 cikin 100 na GDPn kasar.

Mahakuntan kasar Sin sun shafe shekaru hudu a jere, tun daga shekarar 2012 suna zuba sama da kaso 4 cikin 100 na GDPn kasar a sashen ilimi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China