in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci Amurak da ta dakatar da jibge na'urorin kakkabo makaman masu linzami a kasar Koriya ta kudu
2016-11-04 20:50:32 cri
Rahotanni na cewa, a jiya Alhamis ne, Vincent Keith Brooks, kwamandan sojojin Amurka dake a kasar Koriya ta kudu ya ce, kasarsa za ta jibge na'urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin Thaad a kasar Koriya ta kudu a cikin watanni 8 ko 10 masu zuwa, watau za a kammala aikin a watanni shida na farkon shekara mai zuwa. Bayanai na nuna cewa, sansanin da za a jibge wadannan na'urori zai fi sansanin Guam girma.

Game da wannan lamarin, a yayin wani taron manema labaru da aka shirya yau Jumma'a a nan Beijing, madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana cewa, bangaren Sin ya sha bayyana matsayinsa kan yadda ake nuna adawa da lamarin, kuma babu abin da zai hana bangaren kasar Sin daukar matakan da za su wajaba na kare moriyar tsaron kanta. Madam Hua ta nemi bangarorin da abin ya shafa da su mai da hankali kan abubuwan da kasar Sin ke kulawa kamar yadda ya kamata, kuma su gaggauta dakatar da shirinsu na jibge na'urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin Thaad. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China