in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon kasar Sin ya bukaci MDD da ta hada kan kasashen duniya wajen tunkarar kalubalen kasa da kasa
2016-10-20 09:42:01 cri
Manzon kasar Sin a MDD Liu Jieyi, ya bukaci majalissar da ta hada kan kasashen duniya, wajen tunkarar kalubalen dake fuskantar duniya a fagen sauyin yanayi, da tsaro, da matsalolin 'yan gudun hijira da na lafiya, yana mai cewa hadin kan daukacin sassan ne kadai zai bada damar cimma burin da aka sanya gaba.

Mr. Liu wanda ya yi wannan tsokaci a jiya Laraba, a taron MDD wanda mai jiran gadon majalissar Antonio Guterres ya halarta, ya kara da cewa akwai bukatar MDDr ta tallafawa kasashen duniya, wajen bada kariya ga rukunonin mutane dake da rauni. Daga nan sai ya yiwa majalissar fatan samun nasarori a ayyukan da ta sanya gaba, yana mai cewa ko shakka babu, kasar Sin za ta ci gaba da bada gudummawar da ta dace da kudurorin majalissar na bunkasa tsaro, da samar da ci gaba mai dorewa, tare da inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen duniya.

Kaza lika Mr. Liu ya yi fatan MDDr za ta kara himma, wajen ganin an samu nasarar fadada hadin gwiwa tsakanin kasashen duniya, bisa tsarin shugabanci mafi dacewa, wanda zai bada damar cimma moriyar juna bisa adalci. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China