in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karar da Amurka za ta kai gwamnatin Saudiya sakamakon hadarin watan Satumba ba alheri ba ne
2016-09-30 10:46:06 cri
A jiya Alhamis 29 ga wata ne, ma'aikatar harkokin wajen Saudiya ta fitar da wata sanarwa da ke gargadi cewa, kudurin da majalisar dokokin kasar Amurka ta zartas wanda ke nuna goyon bayan iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata sakamakon hadarin ranar 11 ga watan Satumba da su kai karar gwamnatin Saudiya, zai haifar da mummunan sakamako ga kasashen duniya, musamman kasar Amurka.

A ranar Laraba ne, majalisu biyu na Amurka suka shure kujerar nakin shugaba Barack Obama bisa yawancin kuri'un da aka jefa. Shi dai Obama ba ya goyon bayan iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata su kai karar gwamnatin Saudiya. Sai dai wasu iyalan wadanda suka mutu sakamakon hadarin na ranar 11 ga watan satumba suna ganin cewa, kungiyar Al-Qaeda tana samun kudadenta ne daga kasar Saudiya, a saboda haka, ya sa dole ne gwamnatin Saudiya ta dauki alhakin abin da ya faru.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China