in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaminstan Sin ya kai ziyarar aiki a yankunan kogin Yangtse da kogin Huai
2016-07-07 11:23:03 cri
Tun daga ranar 5 ga wata, zuwa jiya Laraba, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya ci gaba da kai ziyarar aiki a birnin Fuyang na lardin Anhui, da birnin Yueyang dake lardin Hunan, da kuma birnin Wuhan na lardin Hubei domin yin bincike kan yadda ake aiwatar da ayyukan yin rigakafi da yaki da ambaliyar ruwa da kuma ayyukan ceto da taimakawa mutanen da bala'in ya shafa dake yankunan kogin Yangtse da kogin Huai.

Li Keqiang ya ce, watan Yuli da watan Agusta su ne muhimmin lokacin gudanar da aikin yin rigakafi kan ambaliyar ruwa, ya kamata a mai da hankali sosai kan ayyukan yin rigakafi da yaki da ambaliyar ruwa, haka kuma ya bukaci hukumonin da abin ya shafa su yi hadin gwiwa yadda ya kamata domin gudanar da ayyukan gaggawa, yayin aiwatar da aikin yaki da ambaliyar ruwa da aikin ceto yadda ya kamata.

Kaza lika ya ce, tsaron madatsar ruwa da aka gina ta da duwatsu da kuma tsaron matarin ruwa suna da muhimmanci wajen yin rigakafi kan ambaliyar ruwa, ya kamata a gudanar da bincike a wurare cikin lokaci, yayin da yin aikin shiryawa bisa yanayin da ake ciki yadda ya kamata, ta yadda za a tabbatar da tsaron yankin.

Bugu da kari, ya ce, ya kamata a karfafa aikin bincike da yin rigakafi kan hadari a yankunan da bala'in ya shafa domin kiyaye tsaron al'ummomin kasar, kana ya kamata hukumar kudi ta gwamnatin kasar ta gaggauta samar da kudaden yin rigakafi da yaki da ambaliyar ruwa ga wuraren da bala'in ya shafa, da kuma ba da jagoranci kan ayyukan samar da bayanan gargadi, da shirya kayayyakin agaji, da tura ma'aikata zuwa wurare da dai sauransu ta yadda za a iya cimma nasarar yaki da wannan bala'i na bana cikin hadin gwiwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China