A yau Litinin ne, aka kaddamar da dandalin tattaunawar Davos na yanayin zafi a birnin Tianjin na Sin, inda firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gabatar da jawabi, tare da jaddada cewa, yanzu tattalin arzikin kasar yana cikin muhimmin ganiyarsa, ta yadda za a kawo gyare-gyare ga tsarin tattalin arzikin kasar, domin kara zabarar da ci gaban tattalin arzikin. Sa'an nan za a kara mai da hankali a kan kirkire-kirkire domin zama jagora ga ci gaban tattalin arziki.
Ya ce, babu wasu manyan sauye-sauye ga manyan fannonin tattalin arzikin kasar, kuma tabbatar da dorewar manufofin da suka shafi manyan fannonin tattalin arzikin kasar. Bana Sin za ta cimma babban burinta na raya tattalin arziki da zamantakewar al'ummarta.(Fatima)