Cikin sabbin yan wasan kasar na bana akwai dan wasan gaba Lorenzen Melvyn, wanda ke buga wa kungiyar Werder Bremen ta Jamus kwallo, ya kuma bayyana farin cikin sa game da samun damar bugawa babbar kungiyar kasar sa wasa a karon farko.
Uganda na matsayi na biyu a rukunin D da maki 7, inda take biye da Burkina Faso, wadda ta doke Uganda da ci daya da nema, a wasan su da ya gabata.
Yanzu haka dai Uganda na bukatar lashe wasannin ta biyu da za ta buga da Botswana da Comoros, kafin ta samu gurbin buga gasar nahiyar Afirka ta AFCON wadda za a gudanar badi a kasar Gabon.(Saminu Alhassan)