in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fidda sakamakon wuraren da ke da karfin samun bunkasuwa a shekarar 2016
2016-05-31 15:23:14 cri
A jiya Litinin ne, kwalejin nazarin harkokin gudanarwa ta Lausanne dake kasar Switzerland ta fidda sakamakon jerin wuraren da ke da karfin samun bunkasuwa a duniya a shekarar 2016,inda yankin Hong Kong na Sin da Switzerland, da Amurka suke kan gaba.

Kwalejin na Lausanne da ke kasar Switzerland ya yaba gogayyar yankin Hong Kong na Sin, yana mai imanin cewa, yankin Hong Kong na da ingantattun tsarin bankuna da hada-hadar kudi, da manufofin da za su karfafa kirkire-kirkire, da tsarin biyan haraji mai kyau. Ban da wannan kuma, yankin na Hong Kong ya yi fice wajen gudanar da kasuwanci, shi ya sa tattalin arzikin yankin ya samu bunkasuwa sosai.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China