160512-Najeriya-za-ta-buga-wasannin-sada-zumunta-da-Mali-da-Luxembourg-zainab.m4a
|
Wasannin dai sun hada da Najeriya da Mali wanda za a buga a kasar Faransa, tuni kuma aka gayyaci 'yan wasan Najeriyar su 26 domin bugawa Super Eagles din wannan wasa.
Kaza lika Najeriyar za ta buga wani wasan na sada zumunta da kasar Luxembourg a ranar 1 ga watan Yuni mai zuwa. Kocin kungiyar ya ce koda yake tawagar kungiyar na kunshe da tsaffin 'yan wasan ta, amma duk da hakan za a baiwa matasan 'yan wasa damar nuna ta su basirar a yayin wasannin.(Saminu Alhassan)