A cewar sakatare janar na kungiyar NFA Barry Rukoro, kaciyan 'yan wasan Ricardo Mannetti ne ya zabo 'yan wasan bayan kammala wasan sada zumanta na cikin gida.
Yan wasan zasu tashi zuwa kasar ta Ghana ne, kuma zasu samu horo na musamman domin shiga gasar wasannin share fage ta AFCON 2017 inda zasu kara da Niger a ranar 4 ga watan Yuni da kuma gasar COSAFA Castle Cup tsakanin ranakun 18 zuwa 25 ga watan Yuni.
Da safiyar ranar Talata ne dai tawagar 'yan wasan ta tashi zuwa kasar Ghana, inda ake saran dawowarsu a ranar 23 ga watan Mayu, inda zasu hadu da sauran 'yan wasannin kungiyar dake zaune a kasashen ketare domin samar da babban kungiyar 'yan wasa.(Ahmad Fagam)