in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Siasia ya sanya Owolabi cikin jerin sunayen 'yan wasan da suke da damar zuwa Rio Olympics
2016-05-05 18:57:21 cri
Babban koci mai horar 'yan wasan kungiyar kwallon kafan Najeriya Samson Siasia, ya sanya Olajide Samuel Owolabi, dan wasan gaba na kulob din Nyokobing na kasar Denmark, cikin jerin sunayen 'yan wasan da za su gwada fasahar su a kungiyar kwallon kafar kasar, gabannin wasannin Olympics da zai gudana a birnin Rio na kasar Brazil a wannan shekara.

Kafin hakan Siasia ya riga ya gabatar da jerin sunaye mai kunshe da 'yan wasa 60 ga hukumar kwallon kafar Najeriya NFF, sai dai har ya zuwa yanzu yana ci gaba da kara wasu 'yan wasan cikin jerin sunayen, da nufin samun fitattun 'yan wasa mafiya dacewa, wadanda za su halarci wasannin Olympics a matsayin 'yan kwallon Najeriya.

Owolabi mai shekaru 21 a duniya, ya taba samun horo cikin kungiyar ta Najeriya kafin gasar All Africa Games ta shekarar 2015, da gasar AFCON ta 'yan kasa da shekaru 23, duk da cewa bai samu halartar gasannin ba a karshe, sakamakon yadda kulob din sa ya hana shi damar shiga gasar ta nahiyar Afirka.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China