A yau Laraba ne, gwamnatin jihar Katsina da ke Najeriya ta kira wani taron manema labarai a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya.
160427-gwamnan-Katsina-murtala.m4a
|
A jawabinsa yayin taron, gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ya yi bayani kan kokarin da gwamnatinsa ke yi don jawo hankalin masu zuba jari, da yadda za a inganta harkokin hako ma'adinai, yawon shakatawa, makamashi,samar da ababen more rayuwar jama'a da sauran batutuwa.
Wakilinmu da ke Najeriya Murtala ya halarci taron ga kuma karin bayanin da ya aiko mana.