in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana za ta kara da habasha a gasar kwallon kafa ta 'yan kasa da shekaru 20
2016-04-27 17:03:34 cri

Kungiyar kwallon kafa ta matasa 'yan kasa da shekaru 20 ta Ghana wato Black Satellites, za ta kara da takwarar ta ta kasar Habasha, a zagaye na biyu na share fagen buga gasar nahiyar Afirka da za a gudanar badi a kasar Zambia.

Tuni dai Habasha ta doke Somalia da jimillar kwallaye 4 da 1, bayan kammala wasan su na Juma'ar da ta gabata, inda kuma za su fafata da Black Satellites ran 20 ga watan Mayu a birnin Addis Ababa a wasan farko, kana su sake haduwa a wasa na biyu ran 10 ga watan Yuni a birnin Accra. Duk kungiyar da ta yi nasara a wannan wasa kuma za ta hadu da ko dai Tunisia ko Senegal a wasa na gaba.

Kungiyoyi 7 da suka shige gaba, za su kece raini a gasar zakarun nahiyar da za ta gudana tsakanin ranekun 26 da watan Fabarairu zuwa 12 ga watan Maris na shekarar mai zuwa a Zambia. Kaza lika kungiyoyin da suka kai ga wasan kusa da na kusan karshe su 8, su ne za su wakilci nahiyar a gasar duniya ta shekarar 2017, ta 'yan kasa da shekaru 20 wadda hukumar FIFA ke shiryawa.

A bara Ghana ce ta uku yayin gasar nahiyar ta Afirka wadda ta gudana a kasar Senegal. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China