in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin kiyaye zaman lafiya na 14 da kasar Sin ta tura ma kasar Liberia ya samu lambar yabo ta MDD
2016-04-21 11:01:47 cri
Tawagar musamman ta MDD dake kasar Liberia ta ba da lambar yabo ga rukunin kiyaye zaman lafiya na 14 da kasar Sin ta tura ma kasar a shekaran jiya Talata a birnin Monrovia, domin nuna yabo ga gudummowar da ta yi wajen aikin kiyaye zaman lafiya. Dukkan 'yan sanda 12 na rukunin sun samu lambobin yabo na kiyaye zaman lafiya.

A gun bikin karramawar, mataimakin wakilin babban sakataren MDD mista Valdemar ya nuna babban yabo ga 'yan sandan kasar Sin kan ladabtarwa da kyakyawar fasaha a fannin aiki da suke da su.

A lokacin da 'yan sandan rukunin kiyaye zaman lafiya na 14 na kasar Sin suke aiki a kasar Liberia, sun yi kokarin aiki a fannonin kiyaye zaman lafiya, da yin bincike, da yaki da miyagun kwayoyi, da kuma sauransu, a daidai lokacin da aka fuskanci kalubalen cutar Ebola. Ban da haka kuma, sun kare moriyar Sinawa da kuma kamfannonin Sin a can yadda ya kamata, sun ba da muhimmiyar gudummowa wajen kiyaye zaman lafiya a kasar Liberia da inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Liberia.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China